Matthew 23

1Sai Yesu yayi wa taron da alamajiransa magana. 2Ya ce, “Marubuta da Farisawa suna zaune a mazaunin Musa. 3Don haka, duk abinda suka umarceku kuyi, kuyi wadannan abubuwa ku kuma kiyaye su. Amma kada kuyi koyi da ayyukansu, gama suna fadar abubuwa amma kuma ba su aikata su.

4I, sukan daura kaya masu nauyi, masu wuyar dauka, daga nan su dauka su jibga wa mutane a kafada. Amma su kan su baza su mika danyatsa ba su dauka. 5Duk ayyukan su suna yi ne don mutane su gani, suna dinka aljihunan nassinsu da fadi, suna fadada iyakokin rigunansu.

6Su na son mafifitan wuraren zama a gidan biki, da mafifitan wuraren zama a majami’u, 7da kuma gaisuwar musamman a wuraren kasuwanci, a kuma rika ce da su ‘mallam.’

8Amma ba sai an kira ku ‘mallam, ba’ domin malami daya kuke da shi, ku duka kuwa ‘yan’uwan juna ne. 9Kada ku kira kowa ‘Ubanku’ a duniya, domin Uba daya ne ku ke da shi, kuma yana sama. 10Kada kuma a kira ku malamai, saboda malamin ku daya ne, shi ne Almasihu.

11Amma wanda yake babba a cikin ku zaya zama bawanku. 12Duk wanda ya daukaka kansa za a kaskantar dashi. Duk wanda ya kaskantar da kansa kuma za a daukaka shi.

13Amma kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kun toshewa mutane kofar mulkin sama. Baku shiga ba, kuma ba ku bar wadanda suke so su sami shiga ba. 14kaiton ku marubuta da Farisawa, domin kuna hallaka gwauraya - 15Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kuna tafiya ketaren tekuna da kasashe domin samun almajiri daya tak, in kwa kun samu kukan mai da shi biyunku danwuta.

16Kaiton ku, makafin jagora, kuda kuke cewa, Kowa ya rantse da Haikali, ba komai. Amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, rantsuwarsa ta daure shi.’ 17Ku wawayen makafi! wanene yafi girma, zinariyar ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar?

18Kuma, ‘Kowa ya rantse da bagadi, ba komai bane. Amma duk wanda ya rantse da baikon da aka dora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.’ 19Ku makafi! Wanene yafi girma, baikon ko kuwa bagadin da yake kebe baikon ga Allah?

20Saboda haka, duk wanda ya rantse da bagadi, ya rantse da shi da duk abinda ke kansa. 21Kuma duk wanda ya rantse da Haikali ya rantse dashi da kuma wanda yake cikin sa. 22Kuma duk wanda ya rantse da sama, ya rantse da kursiyin Allah da kuma wanda yake zaune akai.

23Kaiton ku Farisawa da marubuta, munafukai! Kukan fitar da zakkar doddoya, da karkashi, da lamsur, amma kun yar da al’amuran attaura mafi nauyi-, wato, hukunci, da jinkai da bangaskiya. Wadannan ne ya kamata kuyi, ba tare da kunyi watsi da sauran ba. 24Makafin jagora, ku kan burtsar da kwaro dan mitsil, amma kukan hadiye rakumi!

25Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! kuna wanke bayan moda da kwano, amma aciki cike suke da zalunci da keta. 26Kai makahon Bafarise! Sai ka fara tsarkake cikin modar da kwanon domin bayansu ma su tsarkaka.

27Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar kasa kuke, masu kyaun gani daga waje, daga ciki kuwa sai kasusuwan matattu da kazanta iri iri. 28Haka nan kuke a idanun mutane ku adalai ne, amma a ciki sai munafunci da mugun aiki.

29Kaiton ku marubuta da Farisawa, munafukai! Ku kan gina kaburburan annabawa, kuna kuma kawata kaburburan adalai. 30Kuna cewa, ‘Da muna nan a zamanin Ubanninmu, da bamu basu goyon baya ba wajen zubar da jinin annabawa.’ 31Domin haka kun shaida kanku ku ne ‘ya’yan masu kisan annabawa.

32Sai kuma kuka cika ma’aunin ubanninku! 33macizai, Ku ‘ya’yan ganshekai, Yaya zaku tsere wa hukuncin Gidan wuta?

34Saboda haka, duba, ina aiko maku da annabawa, da masu hikima da marubuta. Za ku kashe wadansun su kuma ku gicciye su. Zaku yiwa wasu bulala a majami’un ku, kuna bin su gari gari. 35Sakamakon hakan alhakin jinin dukkan adalai da aka zubar a duniya ya komo a kan ku, tun daga jinin Habila adali har ya zuwa na Zakariya dan Barakiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikali da bagadi. 36Hakika, Ina gaya maku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.

37Urushalima, Urushalima, keda kika kashe annabawa kika kuma jejjefi wadanda aka turo maki da duwatsu! Sau nawa ne naso in tattaro ki kamar yadda kaza take tattara ‘yan tsakinta cikin fukafukanta, amma kin ki. 38Ga shi an bar maku gidan ku a yashe! Ina dai gaya maku, ba za ku kara gani na ba, sai ran da kuka ce, ‘Albarka ta tabbata ga mai zuwa cikin sunan Ubangiji.”’

39

Copyright information for HauULB